Ƙarshen taron wakilan ƙasashe mafi talauci a dunia a birnin Gao
July 17, 2006A lokacin da ƙasashe 8, masu ƙarfin fada aji a dunia, su ke gudanar da taro a birnin Saint Petesbourg, su kuwa ƙasashe mafi talauci a dunia, sun shirya nasu taron, a birnin Gao da ke arewacin ƙasar Mali.
Wakilai a wannan taron matalauta,sun bayana takaici, a kan ɗaukar sakainar kashi, da shugabanin G8, su ka yi wa harakokin tatalin arziki, da inganata rayuwa a ƙasashen Afrika.
Madame Barry Aminata Toure, shugabar hukumar tattalin arzikin ƙasashen Afrika, CAD Mali, ta yi Allah wadai ,da taron G8 wanda bai haifar da komai ba, a cewar ta, na azo agani.
Sannan tace hatta da shawara da magabatan G 8 su ka yanke bara ta yafe bassusukan da su ka tambayo wasu ƙasashen Afrika, bulla ce , domin har yanzu Afrikawa basu gani ba a ƙass.
Taron gao shine karra na 5 da kasashe matalauta su ka shirya.
A wannan karro, sun tantana a kan matsalolin talauci da gudun hijira.
A ɗazunnan nan ne, aka rufe taron bayan mahaurori masu zafi, akan bassusukan Afrika, da batutuwan yancin ɗan Adam da kuma matsalolin ƙarancin abinci.