1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙungiyar PKK ta kai hari a Turkiyya.

October 21, 2007
https://p.dw.com/p/Bu7w

A Jamhuriya Demokradiyar Kongo, ana ci gaba da ɓarin wuta, tsakanin dakarun gwamnati da na tawayen Jannar Lauren Nkunda.

Tawagar Majalisar Ɗinkin Dunia a wannan ƙasa wato Monuc ta shaidi cewar, a yau faɗa ya ƙazanta, mussamman a arewacin Kivu, a tazara kimlomita kimanin 35 da Goma.

Jannar Lauren Nkunda, ya bayyana aniyar ci gaba da yaƙar gwamnati ,domin ceton yan ƙabilar tusti ,wanda a cewar sa, ke cikin matsanancin hali.

To saidai shugaban ƙasa Joseph kabila, ya maida masa martani da cewar:

„Ba ta kamata Nkunda ya ɗauki kansa, a matsayin garkuwa ga yan ƙabilar tutsi ba.

Wannan bori da ya tada, ya hadasa fitina cikin ƙasa ta hanyar ɓarkewar rikicin ƙabilanci.

Yan tutsi basu cikin haɗari, domin kamar sauran jama´a ƙasa, su na cikin kariyar sojojin gwamnati“.

A ɗaya wajen, gwamnati ta yi kira yan tawayen Mai -Mai masu bata haɗin kai, da su ma su ajje makamai, a yunƙurin samar da zaman lahia mai ɗorewa a ƙasar.