1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ƙungiyar RCD a jahuriya Demokradiyar Kongo ta bayyana shiga zaɓe mai zuwa

March 25, 2006
https://p.dw.com/p/Bv43

Ƙungiyar tawayen RCD, ta Jamhuriya Demokaraɗiyar Kongo, mai samun goyan baya, daga ƙasar Rwanda, ta bayyana shiga zaɓe shugaban ƙasa, da na yan majalisun dokoki, da za a yi ,ranar 18 ga watan juni mai zuwa.

Ƙungiya,r da ta rikiɗa zuwa jam´iyar siyasa, ta bayyana wannan sanarwa a yammancin jiya, a cibiyar ta dake birnin Kinshasa.

Shugabann ƙungiyar Azarias Ruberwa, bugu da ƙari ɗaya daga mataimakan shugaban ƙasa 4, ya bayyana ajje takara a wannan zaɓe.

Da farko RCD, ta yanke shawara ƙauracewa zaɓen, muddun ba a cika, wasu sharuɗɗa, da ta gindaya ba.

A jawabin da yayi ranar 16 ga watan da mu ke ciki, shugaban ƙasa Lauran kabila, yayi alkawarin biyan buƙatocin tsafin yan tawayen.

A ɗaya hannun, sanarwar ta RCD, ta yaba shiga tsakanin da ƙasashe da kuma ƙungiyin ƙasa da ƙasa, su ka yi, ta fannin samar da zaman lahia, a jamhuriya Demokraɗiyar Kongo.

Saidai, a yayin da RCD ta bayyana shiga zaɓen, a yankin Ituri, a na cigaba da gwabaza faɗa, tsakanin yan tawaye da dakatrun gwamnati, tare da haɗin gwiwar dakarun majalisar Ɗinkin ɗunia.