1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙungiyar 'yan adawa a ƙasar Ethiopia ta yi watsi da sakamakon zaɓen yan majalisun dokoki

May 26, 2010

'Yan adawa a ƙasar Ethiopia sun ce zasu buƙaci da a sake gudanar da zaɓuɓukan 'yan majalisun

https://p.dw.com/p/NXoQ
Tawagar wakilai na ƙungiyar Tarayya Turai masu saka ido a zaɓe a ƙasar EthiopiaHoto: DW

Ƙungiyar yan adawa a ƙasar Ethiopia ta yi watsi da sakamakon zaɓuɓukan yan majalisun dokokin da aka gudanar a ranar lahadin da ta gabata ,wanda jam'iyyar Shugaban ƙasar Meles Zenawi ta samu gagarumin rinjaye a kai.Da ya ke magana da kamfanin dilancin labarai na Faransa AFP wani jagoran yan adawar Merara Guidina ya shedda cewa ko ƙaɗan ba zasu amince da sakamakon zaɓen ba, sanan kuma ya ce za su matsa ƙaimi domin a sake shirya wani sabon zaɓen.Wannan sanarwa ta yan adwar ta zone a daidai lokacin da masu saka ido a zaɓen na ƙungiyar tarayya Turai suka ce zaɓen ya na cikke da kura kurai.

Mawallafi: Abdourahamane Hassane

Edita Umaru Aliyu