1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ɓarin wuta tsakanin Isra´ila da Hezbollah a kudancin Labanon

July 25, 2006
https://p.dw.com/p/BupK

An cika sati 2 ciccip da ɓarkewar yaƙi tsakanin dakarun Isra´ila da na Hezbollah.

Da sanhin sahiyar yau, an ci gaba da ɓarin wuta mai tsannani tsakani ɓangarorin 2,a yankin Bint Jbeil, a kudancin Labanon.

Sojojin Isra´ila sun bayyana hallaka yan Hezbollah masu yawa, tare da yin assara sojoji guda 2.

A fagen diplomatia,manyan ƙasashe da ƙungiyoyi na dunia na ci gaba da sappa da marwa, da zumar samun tsaigaita wuta.

Bayan ministocin harakokin wajen France, Jamus da Britania , sakatariyar harakokin wajenAmurika Condoleesa Rice, ta ziyarcir Labanon jiya, inda ta gana da hukumomin ƙasar a game da yaƙin.

Saidai an samu rashin fahintar juna, tsakanin Rice, da shugaban Majalisar dokoki Nabih Berry, bayan ta ambata cewar, ba a za a taɓa samun tsaigaita wuta ba,muddun yan Hezbollah, ba su yi belin sojojin Isra´ila 2, da su ka kama ba.

Nan gaba a yau, Condoleesa Rice, za ta ganawa da Praministan Isra´ila Ehud OLmert, kamin ta wuce zuwa Palestinu.

A ɓanagaren Majalisar Ɗinkin Dunia, a na cikintunani akan hanyoyin aika rundunar shiga tsakani a kudanci Labanon.

Gobe ne idan Allah ya kai mu, a birnin Rome na ƙasar Italia za a buɗa taron ƙasa da ƙasa, wanda kacokam zai maida akala, a kan riginginmun da ya ke wakana a yankin gabas ta tsakiya