1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Afirka ta Kudu: ANC na zaben shugabanninta

Abdourahamane Hassane
December 16, 2017

Jam'iyyar ANC mai mulki a Afirka ta Kudu na shirin zaben sabon jagora wanda zai maye gurbin Jacob Zuma.

https://p.dw.com/p/2pTdg
Nkosazana Dlamini-Zuma tare da Cyril Ramaphosa 'yan takara da za su fafataHoto: Getty Images/AFP/R. Jantilal/G. Kirk

A taron da jam'iyyar ke yi a birnin Johannesburg ana sa ran takara za ta yi zafi, tsakanin mataimakin shugaban kasar Cyril Ramaphosa da Nkosazana Dlamini-Zuma tsohuwar matar Jacob Zuma kana tsohuwar shugabar kwamitin kungiyar tarrayar Afirka. Wannan zabe dai na zuwa daf da lokacin da jam'iyyar ta ANC ake zargin shugabanninta da laifin cin hanci.