1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Afirka ta Kudu ta daukaka kara kan Omar el -Bashir

Kamaluddeen SaniApril 8, 2016

Ma'aikatar shari'a a kasar Afirka ta Kudu ta bayyana cewar gwamnatin kasar za ta daukaka karar da kotun kasar ta yanke kan kuskuran da kasar ta yi na barin Shugaba Omar el-Bashir na Sudan ficewa daga kasar.

https://p.dw.com/p/1ISHG
AU-Gipfel in Addis Abeba, Äthiopien, 31.01.2014 Omar al-Bashir
Hoto: Reuters

Kotun ta ce a hukuncin da ta yanke mahukuntan Afirka ta Kudun na da laifi sakamakon barin shugaban kasar ta Sudan ficewa daga kasar ba tare da sun tsafke shi ba.Shugaba Omar el-Bashir wanda ya halarci taron Kungiyar AU ta Afirka a watan Yunin shekarar da ta gabata ya fice daga Kasar Afirka Ta Kudun ne duk kuwa da takardar sammacen da kotun ICC ta aike da cewar a hukumomin kasar su tsare shi.

Kotun ta ICC ta ce mahukuntan kasar kamata ya yi su kama Shugaban domin sun rattaba a hannu a kan aiwatar da duk wasu tanede-tanden kotun,to amma a nata bangaren gwamnatin Afirka ta Kudun ta ce sun bai wa dukkanin shugabanin da suka halarci taron ne kariya ta fuskar diplomasiya ne.

A yau ne dai Afirka ta kudun ta sake daukaka karar bayan da kotun kasar ta ce ta tafka kuskure kan rashin kama shugaban kasar ta Sudan.