1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Afrika ta kudu ta gaza kamo Shugaba Omar al-Bashir.

Kamaluddeen SaniOctober 5, 2015

Kasar Afrika ta kudu ta bukaci kotun ta kasa da kasa wato ICC data basu karin lokaci don bayar da bayanai kan yadda aka yi suka bar Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ficewa daga kasar ba tare da sun kama shi ba.

https://p.dw.com/p/1Gj1y
Omar al-Baschir ARCHIV
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Elmehedwi

Tun dai shekara ta 2009 kotun dake da mazau nin ta a birnin Hague ta bayar da takardar sammacen kamo Omar al-Bashir a bisa zarge-zargen kisan kiyashi gami da take hakkokin bil Adama a yayin rikicin yankin Darfur na kasar.

Kasar Afrika ta kudu wacce tayi na'am da tande tanaden kotun ta Icc tare da bugar kirgin aiwatar da sammacen to amma ta gaza tsafke Al Bashir a yayin taron shugabanin kasashen Afrika daya gudana a kasar.

Yanzu haka dai mahukuntan Afrikan ta kudun sun ce zasu tinkari kotun ta ICC don neman karin lokacin yin bayanai dalla dalla.