1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Agaji ga mutanen da bala'i ya shafa a Indonisiya

October 28, 2010

Yawan mutanen da bala'in girgizar ƙasa ta ƙarkashin teku da kuma aman dutse ya rutsa da su a Indonisia ya kai 343

https://p.dw.com/p/Pqo3
Agaji ga mutanen yankin Dutsen Merapi daya yi aman wutaHoto: AP

Adadin mutanen da girgizar ƙasa ta karƙashin teku ko kuma tsunami da kuma aman dutse a ƙasar Indonisia ya yi sanadiyyar mutuwar sau ya kai kimanin mutane 343, a yayin  da wasu 400 kuma - har yanzu ba'a san wurin da suke ba, kana wasu dubbannin kuma suka rasa matsugunan su. Fiye da ƙauyuka 13 ne ruwa ya shafe a tsibirin Mentawi dake yammacin Sumatra na ƙasar ta Indonisia bayan wani girgizar ƙasa ta ƙarƙashin ruwan da ta afku a ranar Litinin da ta gabata.

A yanzu dai Jirgin sama na farkon da ke ɗauke da kayayyakin agajin da suka haɗa da tantuna da magunguna da kuma sauran kayayyakin amfanin yau da kullum ya sauka a tsibirin, amma ma'aikatan ceto sun yi amannar cewar har yanzu ba su kai ga wuraren da matsalar  ta fi muni ba. A halin da ake ciki kuma can a yankin kudancin ƙasar, abubuwa sun ɗan lafa bayan aman wutar da dutsen Merapi dake tsibirin Java ya yi a ranar Talata, wanda ya janyo turnuƙewar sararin samaniya da toƙa kana da sanadiyyar mutuwar aƙalla mutane 30.

Tuni dai shugaban ƙasar ta Indonisia ya katse wata ziyarar da yake yi a ƙetare domin sanya ido akan yadda ayyukan  bayar da agaji ga mutanen da matsalar ta rutsa da su ke gudana. 

Mawallafi : Saleh Umar Saleh

Edita : Umaru Aliyu