Agaji zuwa Indonesia
May 28, 2006Opishin ministan harakokin wajen Indonesia, ya bayana ƙaruwar yawan mutanen da su ka rasa rayuka a sakamakon mummunar girgizar ƙasa, da ta rutsa da yankin Java ranar jiya asabar.
Sabuwar ƙiddidigar da a ka gudanar ta bayana cewa, a ƙalla mutane 4.285 su ka riga mu gidan gaskiya.
A halin da ake ciki,Ƙasashe da ƙungiyoyin bada agaji na ƙasa da ƙasa, na ci gaba da kai taimako ga yankin.
Banda asara rayuka,wannan sabuwar masifa, da ta wakana a tsibirin Java, ta raunana mutane fiye da 10. 000 , sannan a kalla mutane dubu 20 sunrasa matsugunai, inji mataimakin shugaban ƙasa Yusuf kalla.
Ya ce a halin da ake ciki, jami´an kulla da agaji, na fuskantar karancin kayan aiki, duk da taimakon gaggawa da ƙasashen dunia ke ci gaba da kaiwa.
Asibitocin ƙasar sun cika sun batse, a yayin,da har yanzu, a ke zaƙullo mutane daga cikin ɓaraguzai.