1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ahmadinejad yace matsin lamban ƙasashen Duniya na karfafa musu gwiwa

April 3, 2010

Iran na shirin gina karin sabbin cibiyoyi biyu na bunkasa sinadran Uraniu

https://p.dw.com/p/Mmfg
Hoto: AP

Shugaba Mahmoud Ahamedinejad ya bayyana cewar, cigaban matsin lamban da Duniya  take wa Iran, da suka haɗa da yiwuwar kakabawa mata sabbin takunkumi, su ne ke daɗa karfafa mata kwarin gwiwa wajen cigaba da shirin inganta makamashinta na nukiliya. Waɗannan kalamai nasa dai sun zo ne, bayan da shugaba Barack Obama ya lashi takobin tabbatar da matsin lamban manyan ƙasashen Duniya akan Tehran, domin ganin cewar tayi watsi da shirinta na bunkasa sinadran Atom, wanda  a cewarsa keda nufin kera makaman Nukiliya. A halin da ake ciki yanzu haka dai, babban jami'in kula da harkokin bunkasa Atom a Iran Ali Akbar Saleh, yace an mikawa shugaba Ahmedinejad bukatun gina sabbin cibiyoyi bunkasa Uranium guda biyu a ƙasar.

Mawallafiya: Zainab Mohammed Edita: Yahouza Sadissou