1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Alasanne Watara ya ce zai tsaya takarar shugaban kasar Ivory Coast

January 15, 2006
https://p.dw.com/p/BvCB

Shugaban babbar jam´iyar adawar kasar Ivory Coast ya ce yana shirin tsayawa takara a zaben shugaban kasar, kuma a shirye ya ke ya koma wannan kasa dake yankin Yammacin Afirka don yiwa jam´iyarsa kamfen. Tsohon FM Allasane Watara ya fadawa jaridar Nord Eclair ta kasar Faranasa cewar lalle zai tsaya takara a karkashin inuwar jam´iyaar RDR. A karkashin shirin wanzar da zaman lafiya na MDD an shirya gudanar da zaben a Ivory Coast ne a karshen watan oktoban bara, amma aka dage saboda matsaloli na kwance damarun sojin sa kai da kuma na shirya zaben. Kawo yanzu dai ba´a sanya ranar gudanar da zaben ba, amma bisa ga dukkan alamu a ciki wannan shekara za´a yi.