1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Al'ummar Musulmin duniya sun soma Azumin watan Ramadan

Salissou Boukari
May 27, 2017

A wannan Asabar din ce Musulmi a sassa daban-daban na duniya suka tashi da Azumin watan Ramadan bayan ganin jinjirin wata da ke nuni da karshen watan Sha'aban, kuma farko watan Ramadan.

https://p.dw.com/p/2dfVZ
Symbolbild Ramadan
Shaidar jinjirin Watan RamadanHoto: picture-alliance/dpa/N. Mounzer

A kasashe da dama na Musulmi, irin su Jamhuriyar Nijar, da Tarayyar Najeriya al'umma sun tashi da azumi a wannan rana ta Asabar, bayan da majalisun koli na addinin Musulunci na kasashen suka tabbatar da ganin jinjirin wata.

A jawabin da ya yi wanda kuma wakilinmu na Sakkwato Faruk Mohammed Yabo ya aiko mana, mai martaba Sarkin Musulmi Sultan Muhammad Sa'ad Abubakar na III da ke a matsayin shugaban majalisar Muslunci ta Tarayyar Najeriya ya yi kira ga jama'a Musulmi da su tashi da Azumin na Ramadan a wannan rana ta Asabar da ke a matsayin ranar daya ga wata.