1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ambaliya: Birtaniya za ta aika da karin sojoji

Gazali Abdou TasawaDecember 28, 2015

Firaministan Birtaniya David Cameroon ya bada sanarwar aikawa da karin sojoji 200 domin kawo dauki a yankunan arewacin kasar da suka fiskanci ambaliya

https://p.dw.com/p/1HUOW
Wetter in Europa Weihnachten 2012 Großbritannien
Hoto: Getty Images

Firaministan Birtaniya David Cameron ya bada sanarwar aikawa da karin sojoji 200 domin kawo dauki a yankunan Arewacin kasar da suka fiskanci ambaliyar da ta biyo bayan ruwan sama kama da bakin kwarya da aka share kwanaki ana shatatawa a yankin.

Da ma dai a baya gwamnatin ta aika da sojoji 300, amma kuma Firaminista Cameron ya ce akwai yiwuwar tura karin wasu sojojin dubu idan dai har matsalar ta kara kamari a nan gaba.

Kafofin yada labaran kasar ta Birtaniya dai sun ruwaito cewa a wannan Litinin Firaministan Cameron zai kai ziyara a yankunan da ambaliyar ta shafa.