1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka ta kara wa'adin dage takunkumin Sudan

Salissou Boukari MNA
July 12, 2017

Shugaban Amirka Donald Trump ya kara wa'adin watanni uku domin dage takunkumin tattalin arzikin da Amirkar ta kakaba wa kasar Sudan tun daga shekara ta 1997.

https://p.dw.com/p/2gOSY
Polen Warschau Rede Donald Trump
Shugaban Amirka Donald TrumpHoto: Reuters/K. Pempel

A ranar 13 ga watan Janairu 'yan kwanaki kafin ya bar kan karagar mulkin kasar ta Amirka, tsohon shugaban kasar Barack Obama ya dage wani bangare na takunkumin da aka kakaba wa kasar ta Sudan tsawon shekaru 20, sannan kuma ya bayar da watanni shida na sa ido ga kasar ta Sudan kafin dage ga baki dayan takunkumin da ke a matsayin wani mataki na ladabtarwa.

Amirka dai na zargin Sudan da laifin daure wa ta'addanci gindi har ma da goyon bayan jagoran kungiyar Al-Qaida Osama Bin Laden. A wannan Laraba ce dai ta kamata wa'adin watannin shida ya cika, amma kuma shugaba Trump ya sake kara wa'adin da watanni uku.