1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amnesty ta ce ana ci gaba da keta hakkin dan Adam a duniya

Mohammad Nasiru AwalFebruary 24, 2016

A rahotonta na bana kungiyar Amnesty International ta yi suka kan tabarbarewar 'yancin dan Adam a duniya baki daya.

https://p.dw.com/p/1I18J
Amnesty International Symbolbild
Hoto: picture-alliance/dpa/W. Kumm

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta ce halin da 'yancin dan Adam ke ciki ya yi muni a duniya baki daya. A lokacin da take gabatar da rahoton shekara shekara na kungiyar a birnin Berlin, babbar sakatariyar Amnesty a Jamus Selmin Caliskan ta ce a cikin kasashe 122 daga cikin 160 da suka gudanar da bincike a cikinsu, sun gano cewa ana azabtarwa ko cin zarafin dan Adam. Kungiyar ta zargi gamaiyar kasa da kasa da rashin yin wani katabus don magance rikice-rikice a duniya. Lura da yawan 'yan gudun hijira miliyan 60 a duniya, kungiyar ta yi kira da a samar da sahihan manufofin kare hakkin dan Adam.