An aiwatar da hukuncin kisa kan mutane 15 a Afghanistan
October 8, 2007Talla
Kasar Afghanistan ta zartas da hukunci kisa kan wasu firsinoni 15 karon farko cikin shekaru 3. Wannan adadin shi ne mafi yawa da aka aiwatar da wannan hukuncin a kan wasu tun bayan kifar da gwamnatin Taliban a shekara ta 2001. Mutanen dai an same su da laifuka iri daban daban ciki har da kisan baki ´yan jarida da wani ma´aikacin MDD da ´yan sanda da fashi da makami da kuma yin garkuwa da mutane. A cikin wata sanarwa tawagar MDD a Afghanistan ta ce da ya fi kyau in da gwamnati ta girmama wata yarjejeniyar da aka cimma akan dakatar da hukunci kisa.