1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bayyana sunayen 'yan takara a Burkina Faso

Abdourahamane HassaneAugust 30, 2015

Majalisar tsara dokokin mulki a Burkina Faso ta bayyana sunayen yan takara na wucin gadi waɗanda zasu tsaya a zaɓen shugaban ɓasar da za a gudanar a cikin Oktoban da ke tafe.

https://p.dw.com/p/1GNzC
Burkina Faso Premierminister Isaac Zida 21.11.2014 Ouagadougou
Hoto: AFP/Getty Images/S. Kambou

A cikin yan takara 22 da aka yi rejista, majalisar ta yi watsi da takarar wasu jama'ar guda shida, a ciki har da ta Ɗan takarar jam'iyyar CDP Congres pour la Democratie ta tsohon shugaban ƙasar wato Blaise Compaoré, ,da kuma wasu shugabannin jam'iyyuin siyasar waɗanda suka yi ƙawance da tsohuwar jam'iyysar da ta yi mulkin wanɗanda suka rufa wa Compaoré, baya ya yi tazarce.

A cikin watan Afrilu da ya gabata aka amince da wata dokar a ƙasar ta haramta wa waɗanda suka goyi bayan tsohon shugaban ya yi wa kudin tsarin mulkin kwaskorima domin tsayawa takara a wa'adi na uku duk kuwa da cewar doka ba ta amince da haka ba kafin daga bisanni titi ya korishi daga mulkin a cikin watan Oktoba shekarar bara.