1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bukaci jan kunnen masu kyamar baki a Jamus

Ahmed SalisuAugust 24, 2015

Shugabannin siyasa a tarayyar Jamus sun ce dole ne a dauki matakan ba sani ba sabo kan masu kyamar baki a kasar.

https://p.dw.com/p/1GKTR
Ausschreitungen in Heidenau Sachsen
Hoto: picture-alliance/dpa/A. Burgi

'Yan majalisar dokokin tarayyar Jamus sun bukaci da a dauki tsauraran matakai kan masu shirya zanga-zangar kyamar baki musamman ma dai 'yan gudun hijira.

Wasu gungun mutane a karshen mako sun yi jerin gwano don nuna rashin amincewarsu da tsugunar da 'yan gudun hijra a garin Heidenau da ke a jihar Saxony da ke gabashin kasar.

Wata 'yar majalisar dokokin jihar ta Saxony Juliane Nagel ta danganta wannan zanga-zanga da aka yi ta kyamar 'yan gudun hijirar da rashin cikakkiyar masaniya ta girke su a jihar.

To sai dai masu adawa da wannan mataki na irin wadannan mutane sun gudanar da zanga-zanga ta lumana don yin Allah wadai da masu kyamar 'yan gudun hijirar inda suka ce su kan suna maraba da 'yan gudun hijirar.