1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An dage zaben shugaban kasa a Somaliya

December 27, 2016

Hukumar da ke kula da zabe a Somaliya ta ce sai a karshen watan Janairu ne zaben shugaban kasa zai gudana bayan da aka dage shi bisa fargabar magudi.

https://p.dw.com/p/2Utoi
Symbolbild Somalia Abstimmung Wahlen
Hoto: imago/Xinhua

Kasar Somaliya ta sake dage zaben shugaban kasa a karo na hudu sakamakon fargabar tursasa wa jama'a da kuma magudin zabe. A gobe Laraba ya kamata a gudanar da zaben, amma kuma wani babban jami'i da ke kula da harkokin zabe na kasar ya bayyana wa manaima labarai cewar za a jinkirtashi har i zuwa karshen watan Janairu.

Bisa ga tsarin kasar Somaliya dai ba kai tsaye talakawa ke zaban shugaban kasa ba. Suna zaben 'yan majalisa ne, wadanda su kuma alhakkin zaban shugaban kasa ya rataya a wuyansu.

'Yan adawan Somaliya sun nuna damuwa dangane da dage-dage zaben na shugaban kasa, lamarin da a cewarsu ke nuna shirin gwamnati na murda wannan zabe.