1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An dakatar da jam'iyyun adawa don ingiza tarzoma

Ramatu Garba Baba
February 8, 2018

Gwamnati kasar Chadi ta sanar da dakatar da wasu jam'iyyun adawa guda 10 bisa zargi na abun da ta kira ingiza tarzoma a tsakanin al'umma.

https://p.dw.com/p/2sJGe
Präsident Tschad - Idriss Déby Itno
Hoto: UImago/Xinhua/C. Yichen

Matakin gwamnati ya biyo bayan zanga zangar kungiyoyin kwadago da jami'yyun suka jagoranta dangane da matakin tsuke bakin aljihu na gwamnatin.

Acewar ministan tsaron Chadin Ahmat Mahamat Bachir, an dakatar da ayyukan jam'iyyun na tsawon watanni biyu, saboda abun da ya kira dalilai na tsaron kasa.

Daura da haka hukumomin kasar sun sanar da haramta jerin gwano da ake shirin yi akan tituna a wannan Alhamis a karkashin jagorancin kungiyoyi masu zaman kasansu da na kwadago da jam'iyyun adawa.