1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yarjejeniyar tsagaita wuta a Sudan ta Kudu ta fara aiki

Suleiman Babayo January 8, 2016

Masu saka ido kan yarjejeniyar tsagaita wuta ta Sudan ta Kudu sun nuna gamsuwa bisa fara aiwatar da yarjejeniyar.

https://p.dw.com/p/1HaVw
Südsudan Riek Machar Salva Kiir
Hoto: picture-alliance/AP Photo/P. Muller

Shugaba Salva Kiir na Sudan ta Kudu ya ba da hakuri kan shekaru biyu da aka kwashe ana yakin basasa da babu kan gado. Kiir ya bayyana haka lokacin da yake bayyana sunayen 'yan majalisa 50 daga bangaren 'yan tawaye gami da amincewa da kafa majalisar ministoci da ta kunshi 'yan tawayen.

Tsohon shugaban kasar Botswana Festus Mogae ke shugabancin hukumar kula da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta, inda aka amince da ministoci 16 daga bangaren gwamnati yayin da 10 za su fito daga bangaren 'yan tawaye.

Cikin watan Disamba na shekara ta 2013 yakin basasa ya barke a Sudan ta Kudu lokacin da Shugaba Salva Kiir ya zargi tsohon mataimakinsa Riek Machar da yunkurin kifar da gwamnati.