An fara azumin watan Ramadan a wasu ƙasashen musulmi
September 12, 2007Talla
Yau a wasu ƙasashen musulmi na dunia a ka fara azumin watan Ramadan.
Rahottani daga Nigeria da Niger sun tabbatar da cewar mafi yawan musulmi a wannan ƙasashen sun tashi da azumin farko a yau laraba.
Saidai a ƙasar Indonesia, wadda ta fi yawan musulmi a dunia, da kuma wasu ƙasashen larabawa, da su ka haɗa da Saudi Arabia , Koweit, Bahrein, Qatar, da haɗɗaɗiyar Daular larabawa, sai gobe a ke fara azumin na Ramadan.
Kamar ko wace shekara, an ka samu rabuwar kanu a game da farkon wannan wata mai tsarki na addinin musulunci.