An gabatar da rahoton Timor Ta Gabas
January 21, 2006Talla
Shugaban yankin Timor ta Gabas Xanana Gusmo ya mikawa babban sakataren MDD Kofi Annan rahoton karshe game da keta ´yancin ´yan Adam a lokacin mulkin Indonesia a yankin. A cikin rahoton, hukumar tsage gaskiya da sansatawa ta tabbatar cewar akalla mutane dubu 102 da dari 800 aka halaka ko kuma suka bace a yankin daga shekarar 1974 zuwa 1999. Wannan adadin ya yi daidai da kashi 10 cikin 100 na ilahirin al´umar yankin Timor ta Gabas. Gusmo ya ce ba manufar kasar sa ce daukar fansa ba, a´a illa kawai adalci take son a nuna. Shugaban ya ce kamar a ATK, dole ne a koyi darasi daga wannan ta´asa don hana sake aukuwar ta a gaba.