An haramta cin kasuwannin kauye a Borno
September 7, 2015Talla
Hukumomin a jihar Borno a shiyar Arewa maso Gabashin Najeriya sun sanar da haramta amfani da dawakai da jakuna a wani mataki na magance hare-haren da mayakan kungiyar Boko Haram ke kaiwa kan dawaki a sassan jihar. Haka kuma hukumomi a jihar sun haram a cin kasuwannin kauye wanda yanzu haka ake zargin ‘yan kungiyar na kaiwa hare-hare tare da kwasar kayayakin abinci da na rayuwar yau da kullum.
Rundunar Sojojin sun ce ya zama dole su dauki wannan mataki ne don kawo karshe ayyukan hare-haren da kungiyar Boko Haram ke kaiwa a yankin a wannan lokaci musamman ganin mayakan sun koma amfani da dawaki da jakuna watakila saboda karancin mai na ababan hawa da suke da su.