1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An harbi fitaccen dan adawa a Tanzaniya

Gazali Abdou Tasawa
September 7, 2017

Wasu mutane da ba a kai ga tantance ko suwa ne ba ya zuwa yanzu sun kai hari da bindiga a gidan mataimakin madugun 'yan adawar kasar Tundu Lissu inda suka jikkata shi. 

https://p.dw.com/p/2jXs3
Tundu Lissu, CHADEMA Oppositionspolitiker Tansania
Hoto: DW/Said Khamis

Rahotanni daga kasar Tanzaniya na cewa wasu mutane da ba a kai ga tantance ko su wane ne ba  sun kai hari da bindiga a gidan mataimakin madugun 'yan adawar kasar Tundu Lissu inda suka jikatashi. 

A cikin wata sanarwa da jam'iyyarsa ta Chadema ta fitar a wannan Alhamis ta ce an harbi mataimakin shugaban nata a ciki da kuma a kafa kuma yanzu haka an garzaya da shi zuwa assibiti rai kwakwai mutu kwakwai. 

Tundu Lissu wanda dan majalisar dokoki ne a kasar ta Tanzaniya dan siyasa ne da ya yi fice wajen sukar lamirin Shugaban kasar tasu John Magufuli. Kuma an kai masa harin ne a da misalin karfe biyu agogon GMT a gidansa da ke a birnin Dodoma babban birnin kasar jim kadan bayan dawowarsa daga zaman majalisa.

Hukumar 'yan sandar birnin na Dodoma ta sanar da soma gudanar da bincike kan wannan batu.