1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An jefi tawagar Macron a Burkina Faso

Yusuf Bala Nayaya
November 28, 2017

Lamarin na faruwa yayin da ake tsammanin Shugaba Emmanuel Macron na Faransa zai yi babban jawabinsa a jami'ar birnin Ouagadougou.

https://p.dw.com/p/2oO7G
Burkina Faso - Emmanuel Macron mit Roch Marc Chiristian Kabore
Hoto: Reuters/P. Wojazer

Mai magana da yawun gwamnatin Faransa ya bayyana cewa an jefi motar mambobin wata tawaga da ke bin bayan Shugaba Emmanuel Macron a ziyararsa zuwa Burkina Faso.

Bruno Roger-Petit ya bayyana a shafinsa na Twitter cewa lamarin ya faru ne a yayin da a bangare guda kuma Shugaba Macron da takwaransa Roch Marc Christian Kabore na can suna tattaunawa. Har iala yau lamarin na faruwa yayin da ake tsammanin Macron zai yi babban jawabinsa a jami'ar Ouagadougou, duk da fargaba da ake da ita ta samun zanga-zanga ta masu bore. Gwamnatin ta Burkina Faso dai ta bada umarni a rufe makarantu don samun sauki na samar da tsaro da rage kai kawo ababan hawa.