1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kada kuri'ar zaman iyalan baki a Jamus

Yusuf Bala Nayaya
February 1, 2018

Majalisar wakilan Jamus ta kada kuri’a kan sake maido da dokar da za ta ba da dama ga ‘yan gudun hijira su kawo iyalansu zuwa kasar.

https://p.dw.com/p/2rydZ
Bundestag Abstimmung Familiennachzug Merkel
Batun 'yan gudun hijira na da muhimmanci a siyasar JamusHoto: picture-alliance/AP/M. Sohn

Daga ranar daya ga watan Agusta iyalan  bakin hauren 1,000 ne za a rika basu damar zuwa Jamus a duk wata, muddin dai suna da alaka ta kai tsaye da ‘yan gudun hijirar da ke zaune a kasar ta Jamus.

Wannan sabuwar dokar da jam'iyyar masu ra'ayin mazan jiya ta Angela Merkel CDU da jam'iyyar SPD suka gabatar, ‘yan majalisa 376 ne suka amince da ita yayin da 248 suka ki aminta. A cewar ministan cikin gidan Jamus Thomas de Maiziere wannan mataki ne me muhimmanci.

A watan Maris na shekarar 2016 ne dai gwamnatin ta Jamus ta tsayar da ba da dama ga ‘yan gudun hijira da ke da kwarya-kwaryar izinin zama su hade da iyalansu. Jamus dai ta yi marhabun ga 'yan gudun hijira 890,000 a shekarar 2015.