An kafa dokar hana fita a yankuna da dama na Iraqi, gabannin yanke wa Saddam Hussein hukunci da kotu za ta yi yau a birnin Bagadaza.
November 5, 2006Sa’o’i kaɗan kafin buɗe shari’ar tsohon shugaban ƙasar Iraqi, Saddam Hussein, yau a birnin Bagadaza, inda ake sa ran kotun za ta yanke masa hukunci, gwamnatin Iraqin ta kafa dokar hana fita a yankuna da dama na ƙasar. Ta kuma soke duk hutun jami’an rundunar sojin ƙasar, saboda fargabar idan an yanke wa Saddam hukuncin kisa, za a yi tashe-tashen hankulla a ƙasar.
Lauyoyin Saddam ɗin dai sun ce a tattaunawar da suka yi da shi jiya asabar, ya bayyana musu cewa a shirye yake ya mutu da daraja kuma ba da wata fargaba ko tsoro ba. Ya kuma ce Amirka za ta sha kaye a Iraqin, kafin ta janye dakarunta daga ƙasar cikin kunya.
A ci gaba da tashe-tashen hankullan da ake addabar birnin Bagadazan dai, ma’aikatar harkokin cikin gidan Iraqin ta ce mutane 7 ne suka rasa rayukansu jiya daddare, sa’annan wasu 20 kuma suka ji rauni, a wani harin rokoki da aka kai a unguwar Adhamiyya.