1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai hare-haren ta'addanci a Mali

Abdourahamane HassaneNovember 28, 2015

Rahotannin daga Mali na cewar wasu 'yan bindiga su kai harin rokoki a cibiyar rundunar kiyaye zaman lafiyata ta Majalisar Ɗinkin Duniya watau MINUSMA da ke a garin Kidal a yankin arewacin ƙasar.

https://p.dw.com/p/1HE0m
Mitglieder UN Stabilisation Armee Mali Minusma Bastille Tag Paris Frankreich
Hoto: Getty Images/AFP/L.Bonaventure

Wani babban jami'in rundunar ya tabbatar da cewar 'yan bindiga sun kai hare-haren da sahin safiyar wannan Asabar inda suka kashe sojoji biyu da farar hula ɗaya kana wasu mutane 20 suka samu raunika. Wannan hari, na zuwa ne kwanaki kadan bayan harin da kungiyar alqaida reshen magreb AQMI, ta kai a makon jiya a cikin Otel Radisson da ke birnin Bamako wanda a cikin kusan mutane 20 suka rasa rayukansu