An kai hare-haren ta'addanci a Mali
November 28, 2015Talla
Wani babban jami'in rundunar ya tabbatar da cewar 'yan bindiga sun kai hare-haren da sahin safiyar wannan Asabar inda suka kashe sojoji biyu da farar hula ɗaya kana wasu mutane 20 suka samu raunika. Wannan hari, na zuwa ne kwanaki kadan bayan harin da kungiyar alqaida reshen magreb AQMI, ta kai a makon jiya a cikin Otel Radisson da ke birnin Bamako wanda a cikin kusan mutane 20 suka rasa rayukansu