1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai sabbin hare-hare a kudancin Afghanistan

Ibrahim SaniDecember 8, 2007
https://p.dw.com/p/CZ2Y

Dakarun sojin Afghanistan bisa jagorancin sojin tsaro na Nato, sun ƙaddamar da wasu sabbin hare-hare a kudancin ƙasar. Matakin ya zo ne a ƙoƙarin ƙwato garin Musa Qala ne, dake hannun tsagerun ƙungiyyar Taliban. A yanzu haka dai an shafe kusan watanni goma ke nan garin na Musa Qala na hannun tsagerun na Taliban. Ana zargin cewa tsagerun na amfani da garin ne, a matsayin cibiyar hada-hadar muggan ƙwayoyi. Yankin dai na Helmand dake kusa da garin Musa Qala, yankine da ya yi ƙaurin suna wajen shuka muggan kwayoyi da kuma hada-hadarsu.