1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kara tsananta matakan tsaro a birnin London

June 30, 2007
https://p.dw.com/p/BuHW
´Yan sanda a London babban birnin kasar Birtaniya sun tsananta binciken da suke yi don gano wadanda ke da hannu a yunkuri kai harin bam a birnin. Rahotanni daga London sun ce yanzu an fara tuntubar hukumomin wasu kasashen waje a cikin binciken. A dai halin da ake ciki an tsaurara matakan tsaro inda kuma ´yan sanda suka tsananta binciken ababan hawa a birnin. Kwararrun masana harkokin tsaro sun ce shirin kai hare haren na da kama da aikin kungiyar ´yan ta´adda ta al-Qaida.