1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An Kashe mayakan IS a Masar

July 9, 2017

'Yan sanda a Masar, sun kashe wasu da ake ganin 'yan bindigan IS ne su 14, a wani farmaki da suka kai har tungarsu 'yan jihadin a gabashin lardin Islamiyya.

https://p.dw.com/p/2gEhY
IS Kämpfer Videostill
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Mahukunta a Masar, sun ce sun halaka 'yan bindigan IS din ne su 14, a farmaki da suka kai har maboyar 'yan jihadin a gabashin lardin Islamiyya. Sanarwar masu kayan sarkin na zuwa ne kasa da sa'o'i 48 da IS ta kaddamar wani hari a kan sojin kasar.

A cewar ministan harkokin cikin gidan kasar ta Masar, 'yan sandan sun afka wa mayakan na IS ne a gabashin lardin Islamiyya yankin da IS din ke da sansani a can. Gwamnatin Masar ta kuma ce biyar daga cikin 'yan bindigan, na cikin jerin wadanda da ma take nema 'ruwa a jallo'.

Ko a Juma'ar da ta gabata ma dai mayakan na tarzoma sun kaddamar da hare-hare a wasu shingayen bincike da ke yankin Sinai, inda suka yi ruwan Bama-Bamai gami da albrusai, sai dai jami'ai sun yi ikirarin kashe su da dama.