1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kwashe bakin hauren a Calais na Faransa

October 26, 2016

Mahukunta sun tabbatar dab kwashe daukacin bakin hauren da ke Calais na Faransa masu neman shiga Birtaniya.

https://p.dw.com/p/2RkDu
Calais Räumung
Hoto: picture-alliance/dpa/E. Laurent

An kwashe daukacin bakin haure da suka kafa sansani a tashar jiragen ruwan Calais da ke arewacin Faransa. Jami'an karamar hukumar sun ce haka ya biyo bayan gobarar da aka samu a sansanin bakin haure yayin da ake kwashe su zuwa wasu sassan kasar domin su neman mafaka ko kuma su koma kasashensu.

Fiye da mutane 5,000 suka yada zango a sansanin na Calais bisa tunanin watan-wata rana za su samu shiga Birtaniya ta barauniyar hanyar. Faransa ta nemi Birtaniya ta karbi daukacin yara da suke su kadai a sansanin, amma Birtaniya ta ce za ta amince da rabi.