1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An rantsar da Bashar Al Assad a wani saban wa´adi na shekaru 7

July 17, 2007
https://p.dw.com/p/BuG8

Majalisar dokokin Syria ta rantsar da shugaban kasa bashar Al-Assad, a wani saban wa´adin mulki na shekaru 7.

A jawabin da ya gabatar gaban yan majalisar, Bashar Al Assad ya bayyana aniyar sa, ta ci gaba da gudanar da ayyukan kyauttata makomar al´lummar Syria da kuma kare yancin ƙasar daga barazanar da ta ke fuskanta daga wasu ƙasashen ƙetare.

A game da rikicin Isra´ila da Syria shugaba Al Assad ya, ya yi kira ga hukumomin Tel Aviv, su bayyana ƙarara aniyar su, ta samar da zaman lahia a mai ɗorewa.

Tun shekara ta 2000 tantanwar tsakanin ƙasashen 2 ta watse baran-baran.

Syria na buƙatar sake mallakar yankunan ta, na tuddan Golan, da Israi´la ta mamaye, tun shekara ta 1967.

A yayin da ya ke huruci a game da saban wa´adin mulkin na Bashar Al Assad, Wadah Abdu Rabo, shugaban jaridar Al watan mai zaman kanta a Syria na mai cewa.