1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An rantsar da shugaban gwamnatin wucin gadi na kasar Bangladesh

January 12, 2007
https://p.dw.com/p/BuUi

An rantsar da tsohon shugaban babban bankin Bangladesh a matsayin sabon shugaban gwamnatin wucin gadin kasar. Fakhruddin Ahmed wanda tsohon ma´aikacin bankin duniya ne, ya yi rantsuwar kama aiki ne a wani buki da aka yi a fadar shugaban kasa dake birnin Dhaka. Shi ya maye gurbin Iajuddin Ahmad wanda a jiya alhamis ya yi murabus. Kafin ya sauka ya shugaba Ahmad ya dage zaben ´yan majalisar dokoki da ake shirin gudanarwa a ranar 22ga watan nan na janeru sakamakon zanga-zangar da kawance ´yan adawa ya shirya. ´Yan adawar na zargin cewa za´a tabka magudin zabe. A kuma halin da ake ciki an girke karin dakarun soji da na ´yan sanda a fadin kasar ta Bangladesh bayan dokar ta baci da aka kafa.