1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An rufe jaridar Zaman a Turkiyya

Abdourahamane HassaneMarch 5, 2016

'Yan sanda a Turkiyya sun rufe wata jarida watau Zaman wacce ke kusa da 'yan adawar kasar.

https://p.dw.com/p/1I7hs
Türkei Istanbul Protest Übernahme Zeitung Zaman
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Suna

'Yan sanda a ƙasar Turkiyya sun yi amfani da barkono tsohuwa da kuma kulake,wajen tarwatsa wasu jama'ar da suka yi dandanzo a bakin wata jaridar mai sunan zaman waɗanda jama'ar suka so su hana 'yan sandar rufe jaridar.

Kotu dai ta ba da umarni da a rufe jaridar wacce ake bugawa sati-sati.Gwamnatin Turkiyyar na zargi jaridar da haɗa baki da wani ɗan siyasar wani shehin mallami mai wa'azi da ke hijira a Amirka da nufin tayar da fitina a ƙasar.To sai dai da yake mayar da martanin babban editan jaridar ya ce gwamnatin na takura musu sakamakon sukarta da suke yi a cikin sharhunan da suke rubutawa.