An sallami wakilan Hamas daga gwamnatin hadaka
August 18, 2007Talla
Shugaban yankin Palasdinawa Mahmud Abbas, ya katse dangantar dake tsakanin gwamnatin sa da kungiyyar masu tsatsauran ra´ayi ta Hamas.Al´amarin ya faru ne bayan da shugaban ya sallami duk wani dan kungiyyar, dake rike da wani babban mukami a cikin gwamnatin ta Palasdinu .Tuni dai kungiyyar ta Hamas ta mayar da martanin hawa kujerar naki a game da wannan mataki.Kafin dai daukar wannan mataki, kungiyyar ta Hamas nada mukamai kusan dari biyu a cikin gwamnatin hadakar, da shugaba Abbas kewa jagoranci.