1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sami asarar rayuka a Kenya

August 10, 2017

Akalla mutane hudu sun mutu, bayan rikicin samun sakamakon farko na zaben shugaban kasa a jiya Laraba.

https://p.dw.com/p/2hy3g
Kenia nach Wahlen Unruhen und Protest
Hoto: Getty Images/AFP/F. Lerneryd

Rahotannin da ke fitowa daga Nairobi babban birnin kasar Kenya, na cewa akalla mutane hudu ne aka tabbatar sun mutu, bayan rikicin samun sakamakon farko na zaben shugaban kasa a jiya Laraba. Hukumar zaben kasar ta bayyana shugaba Uhuru Kenyatta a matsayin wanda kuri'unsa suka fi yawa a galibin kuri'un da aka kidaya. Jagoran adawar kasar Raila Odinga ya yi zargin kutse a na'aurorin hukumar zaben kasar, da kuma ya ce ba zai lamunta da shi ba, lamarin da ya tunzura magoya bayansa nuna fushi a sassan kasar a jiya Laraba.

Gabanin zaben dai an kashe wani babban jami'in hukumar zaben mai kula da sashen adana bayanai, wanda kuma wasu suka ce ba zaii rasa nasaba da zafin zaben ba. Bayanai sun ce 'yan sandan kasar sun yi amfani da karfi musamman ma buda wuta a kan masu zanga-zangar.