1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sami fashewar bututunan mai a kafofin haƙo man fetur a tarayyar Najeriya.

July 13, 2006
https://p.dw.com/p/Buqi
Bakin haure daga Senegal
Bakin haure daga SenegalHoto: AP

A tarayyar Najeriya, an sami tagwayen fashewar bututun mai a wasu kafofin haƙo man fetur na kamfanin Agip da ke yankin Naija-Delta. Jami’an gwamnati sun ce suna tuhumar ’yan ɓata gari ne da janyo fashewar bututun a jihar Bayelsa. Har ila yau dai, babu wanda ya yi ikrarin kai hari a kan kafofin.

Tun farkon wannan shekarar dai, hare-haren da ’yan ta kife suka yi ta kaiwa a kan kafofin hakon man fetur, a yankin na Naija-Delta, ya janyo asarar kusan kashi 20 cikin ɗari, na yawan man garwa miliyan biyu da rabin da Najeriya ke fitarwa a ko wace rana zuwa ƙetare. Wannan rikicin dai, ya janyo hauhawar farashin man fetur a kasuwannin duniya.