1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An soki lamirin kafofin yada labarun Rasha

June 5, 2006
https://p.dw.com/p/BuvJ

A taron ta na shekara shekara dake gudana a birnin Mosko, kungiyar buga jaridu ta kasa da kasa ta yi kakkausar suka ga kafofin yada labarun kasar Rasha. A jawabin bude taron wanda aka yi a gaban shugaba Vladimir Putin, kungiyar ta yi korafin cewa gwamnatin Rasha na kara dora hannunta a aikin watsa labaru na cikin kasar. Kungiyar ta ce hukumomi a birnin Mosko na yada wani yanayi na rashin sanin tabbas tare da matsawa ´yan jarida tace labaru da kansu. Shugaba Putin yayi watsi da wannan zargi da cewa bai da tushe bare makama.