1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An soki manufar ketare ta Syria

December 31, 2005
https://p.dw.com/p/BvEQ

Tsohon mataimakin shugaban kasar Syria Abdel Halim Khaddam yayi murabus daga jam´iyar da ke mulki a kasar. Khaddam wanda ya dade akan mukamin, ya dauki wannan mataki ne jim kadan bayan ya soki lamirin manufar ketare ta Syria karkashin shugaba Bashar al-Assad, wadda ta janyo janyewar dakarun kasar daga Lebanon a cikin watan afrilu. Khaddam ya ce gwamnatin shugaba al-Assad ta tabka kurakurai da dama ciki har da na kokarin kare tsohon shugaban hukumar leken asirin ta a Lebanon Janar Rustom Gahzali. Khaddam ya ce Syria ta yi ta yiwa tsohon FM Lebanon Rafik Hariri barazana tun gabanin harin bam din da ya halaka shi a cikin watan fabrairu. Syria dai ta musanta hannu a kisan tsohon FM na Lebanon, duk da kashin kajin da wani binciken MDD akan kisan ya shafawa jami´an Syria.