1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An tarwatsa 'yan Biafra a Port Harcourt

Mouhamadou Awal BalarabeNovember 10, 2015

'Yan Awaren na Biafra sun gudanar da zanga-zanga a birnin Port Harcout don tilasta wa hukumomi sako wani mambansu. Amma kuma hakarsu ba ta cimma ruwa ba.

https://p.dw.com/p/1H3ge
Karte Biafra Nigeria
Hoto: DW

'Yan sandan kwantar da tarzoma sun yi amfani da harsasan roba da kuma hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa zanga-zangar da masu rajin kafa kasar Biafra suka gudanar a birnin Port Harcourt da ke yankin Kudu maso gabashin Najeriya. Suna nema a sako wani dan aware mai suna Nnamdi Kanu da aka kame tun watan Kktoba sakamakon watsa shirye-shiryen a wata rediyo da suka kafa ba bisa ka'ida ba.

Wasu da suka shaidar da gangami na Biaffra sun bayyana cewar jirage masu saukar angulu sun yi shawaki a sararin samaniyar birnin Port harcourt. sai da kuma kwamishinan 'yan sandan wannan jiha ta Rivers ya karyata rade-raden da ake yayatawa cewa sun yi amfani da karfi wajen tarwatsa 'ya awaren na Biafra.

Irin wannan yunkuri na neman ballewa daga Najeriya ya taba haddasa yakin basasa a baya, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane miliyan daya.