1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi gumurzu tsakanin sojin Isra'ila da Falasdinawa

Abdul-raheem Hassan
May 11, 2017

Hatsaniya ta kaure tsakanin Falasdinawa da sojojin Isra'ila a lokacin da daruruwar mutane ke zanga-zangar nuna goyon baya ga 'yan uwansu da ke yajin cin abinci a gidajen yarin Isra'ila.

https://p.dw.com/p/2cpJZ
Israel Mehr als tausend Palästinenser in israelischer Haft im Hungerstreik | Proteste in Ramallah
Hoto: Reuters/M. Torokman

Wasu daga cikin masu zanga-zangar na bangaren Faladinawa sun samu munanan raunuka bayan da sojojin suka yi maratanin kariya da harsasan roba. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ke maraba da shiga tsakaninn kasashen biyu don sake tattaunar sulhuntasu. A baya-bayannan shugaban Amirka Donald Trump ya bayyana yunkurinsa na ganin ya kawo karshen rashin jituwa tsakanin Isra'ila da Falasdinu.

A tun watan watan Afirilu da ta gabata daruruwan Falasdinawa da ke tsare a gidajen yarin Isra'ila, suka sanar da fara yajin cin abinci bisa rashin kulawa a gidajen kaso. To sai dai Isra'ila ta ce gidajen yarin kasar na cika dukkanin ka'idoji da sharuda.