1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi hatsarin jirgin kasa a Masar

Abdourahamane Hassane
August 11, 2017

Mutane 36 suka rasa rayukansu a arewacin Masar bayan da wasu jiragen kasar guda biyu suka ci karo da juna kusan da birnin Alexandria.

https://p.dw.com/p/2i64V
Busunglück Unfall Zug Ägypten Kairo Kinder
Hoto: Reuters

Kafofin watsa labarai na Masar sun ce hadarin ya faru ne a lokacin da daya daga cikin jiragen, ya tsaya kan hanya bayan ya samu wata yar guntuwar matsala. Jiragen biyu wadanda daya ya taso daga birni Alkahira zuwa Alexandria, kana daya ya fito daga Port Said a kan hanyarsa ta zuwa birnin Alexandria sun ci karo a cikin jeji.