1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi kira da a kawo karshen rikici a arewacin Libanon

May 21, 2007
https://p.dw.com/p/BuKy
A kuma halin da ake ciki wakilin MDD a GTT Terje Roed Larsen ya nuna matukar damuwarsa game da fadan da ake yi tsakanin sojojin Libanon da masu tsattsauran ra´ayin Islama. Larsen ya yi kashedin cewa fadan ka iya rikidewa zuwa wani gagarumin yaki. Bayan wani taro da yayi da shugaban kungiyar kasashen Larabawa Amr Mussa a birnin Alkahira Larsen ya fadawa manema labarai cewa sun yi doguwar tattaunawa game da halin da ake ciki a Libanon. Ya yi kira ga dukkan wadanda abin ya shafa da su nuna halin ya kamata don gano bakin zaren warware wannan rikici.