1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi kira ga Jamusawa da su yaki ayyukan kyamar baki a cikin kasar

May 27, 2006
https://p.dw.com/p/BuwU

Kusan makonni biyu gabanin fara gasar cin kofin kwallon kafa na duniya, SGJ Angela Merkel ta yi kira ga ´yan kasar da su kara himmatuwa wajen yaki da ayyukan masu kyamar baki. Merkel ta fada a birnin Frankfurt cewar bai kamata a jurewa duk wani aiki na kaiwa baki hari ba. Ta ce ba ma kawai a lokacin gasar cin kofin kwallon kafar ba, a´a a kowane lokaci duniya na sa ido akan irin abubuwan dake wakana a cikin kasar ta Jamus. Shugaban hukumar kula da harkokin cikin gida na majalisar dokoki Sebastian Edathy yayi kira da a kara yawan ´yan sanda a gabashin kasar, inda aka fi fama da matsalar nuna wariyar launin fata. A ranakun alhamis da juma´a an kai hare hare iri dabam dabam akan baki a biranen Weimar da Berlin, inda aka yi musu rauni iri dabam dabam.