1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi wata makarkashiyar kai harin ta´addanci a Jamus

August 18, 2006
https://p.dw.com/p/BumM
Jaridar Süddeutsche Zeitung ta nan Jamus ta rawaito cewar an shirya kaiwa kasar wani harin ta´addanci shigen wanda aka kaiwa birnin London a bara. Jaridar ta ce wani bincike da aka yi ya gano cewar wasu bama-bamai biyu da aka gano boye a cikin wasu jakuna a tashoshin jiragen kasa na biranen Dortmund da Koblenz cikin watan jiya, na daga cikin makarkashiyar kai harin. Jaridar mai fita kullum ta rawaito manyan jami´in tsaro da bata ambaci sunansu na bayanin haka. Jaridar ta kuma jiyo daya daga cikin jami´an na cewa karfin bama-baman ka iya janyo mummunar asara kamar yadda aka fuskanta a hare haren ta´addancin da aka kaiwa birnin London a cikin watan yulin bara.