1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana ci gaba da fiskantar rikici a Thailand

May 17, 2010

Fito na fito na ƙasar Thailand ya salwantar da rayukan fararen hula 35 ya zuwa yanzu.

https://p.dw.com/p/NPfm
Hoto: AP

Arangama na ci gaba da gudana tsakanin masu ƙin jinin gwamnatin Thailand da kuma dakarun wannan ƙasa da ke neman dawo da doka da oda.  A kalla fararen hula 35 suka mutu ya zuwa yanzu a faɗan da ya ɓarke tsakanin masu adawa da gwamnatin da Jami'an tsaro.

 Rikicin dai ya mamaye birnin na Bangkok da kewaye, inda ya zuwa yanzu ake cigaba da fito na fito tsakanin dakarun gwamanti da kuma magoya bayan tsohon firaminista.

Gwamantin ta Thailand  ta na ci gaba da karfafa martaninta kan masu zanga-zangar, tare da ƙin  amincewa da shiga tattaunawar da Majalisar Ɗunkin Duniya za ta jagoranta, domin kawo ƙarshen rikicin daya shiga yini na huɗu.

Mawallafi: Mouhamadou Awal Edita: Abdullahi Tanko Bala