1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana ci gaba da kokarin shawo kan rikicin Israela da Lebanon

August 4, 2006
https://p.dw.com/p/Buno

A ranar litinin ne idan mai duka ya kaimu ake sa ran ministocin harkokin wajen kasashen larabawa zasu gudanar da wani taron gaggawa, a birnin Cairo na kasar Masar.

Taron a cewar, mataimakin shugaban kungiyyar,Ahmed Ben Helli, zai tattauna rikicin dake tsakanin Israela ne da kuma kungiyyar Hizbullah.

Ko da a yau juma´a sai da jiragen yakin sama na Israela suka kai wasu hare hare a kudu da kuma arewacin birnin Beirut, wanda hakan yayi sanadiyyar rasuwar mutane fararen hula 40.

A waje daya kuma, dakarun kungiyyar Hizbullah sun shaidar da harba rokoki sama da dari izuwa arewacin kasar Israela a yau din nan, wanda hakan yayi sanadiyyar rayuka uku tare da jikkata wasu da dama.